Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedRundunar sojin Nijeriya za ta murƙushe duk wata barazanar tsaro — CDS...

Rundunar sojin Nijeriya za ta murƙushe duk wata barazanar tsaro — CDS Oluyede

Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Olufemi Oluyede, ya tabbatar da cewa rundunar sojin Nijeriya za ta murƙushe duk wata barazana ga tsaron ƙasa a ko’ina take, yana mai cewa ba za a yi rangwame ga masu tayar da zaune-tsaye ba.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin bikin Ranar Tunawa da Sojoji ta 2026, kamar yadda jaridar The Guardian ta ruwaito.

Janar Oluyede ya jaddada cewa tsaro shi ne ginshiƙin martabar kowace ƙasa, kuma rundunar sojin Nijeriya za ta ci gaba da aiki ba dare ba rana domin kakkabe ‘yan tada ƙayar baya da sauran barazanar tsaro.

Babban Hafsan Tsaron ya kuma nuna godiya ta musamman ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa abin da ya kira jajircewa da kuma samar da sabbin dabaru da goyon bayan da gwamnatin ke bai wa rundunar sojin ƙasa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata