Wednesday, April 8, 2026
HomeUncategorizedSabon tsarin karatu na makarantun firamare zai fara aiki a duk fadin...

Sabon tsarin karatu na makarantun firamare zai fara aiki a duk fadin kasar Nijeriya daga watan Janairun 2025 – Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman

Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman, ya ce sabon tsarin karatu na makarantun firamare zai fara aiki a duk fadin kasar daga watan Janairun 2025.

Da yake gabatar da jawabin sa a wani taron  masu ruwa da tsaki a Abuja a ranar Litinin,FarfesaTahir Mamman  ya bayyana cewa a sabon tsarin karatun, za a bukaci daliban da ke makarantun Firamare da na sakandare su laƙanci  akalla sana’o’i biyu.

Ya ce, yana da kyau sosai dalibai su sami damar kammala makaranta da aƙalla ƙwarewa kan ayyukan hannu biyu domin samun rayuwa mai inganci. 

Ya Kara da cewa wannan wajibi ne da ya shafi dukkan makarantu a Najeriya, na gwamnati da masu zaman kansu, kuma duk makarantu za su aiwatar da shi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata