Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedSarkin Katsina ya sanar da korar shirin AGILE bisa saba ka’idojin Musulunci

Sarkin Katsina ya sanar da korar shirin AGILE bisa saba ka’idojin Musulunci

 
Mai Martaba Sarkin Katsina Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya sanar da korar shirin inganta ilmin ‘ya’ya mata na AGILE daga jihar Katsina.
Mai Martaba Sarkin ya ayyana korar ne ga manema labarai a fadarsa, a lokacin da ya ke wasu nade-naden sarautu a karshen mako.
Jaridar yanar gizo ta Mobile Media Crew ta rawaito Sarkin na cewa, korar shirin ya biyo bayan keta wasu ka’idoji addinin Musulunci da shirin ke kokarin yi a jihar da kuma zargin kokarin bata tarbiyar ‘ya’ya mata da ke karatu a makarantu
Ya ci gaba da cewa shirin na kokarin wuce gona da iri wanda a matsayinsu na iyayen kasa, ba za su lamuncewa hakan a cikin kasa ba.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata