Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedShugaba Tinubu bai saka aikin samar da lantarkin Mambila cikin kasafin kudin...

Shugaba Tinubu bai saka aikin samar da lantarkin Mambila cikin kasafin kudin 2024 ba

Jaridar Daily Trust ta gano cewa a cikin daftarin kasafin kudin shekarar badi, 2024 d shugaba Tinubu ya gabatar wa majalisa, babu kason aikin samar da lantarki a Mambila da ke Gembu jihar Taraba.
Sai dai an ware wa ma’aikatar makamashi da ke kula da sha’anin lantarki kudi Naira milyan 400 don shirya taruka a cikin shekarar ta 2024.
Aikin samar da lantarki na Mambila dai ya haddasa ce-ce-kuce a zamanin gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari, da ake kyautata zaton idan an yi shi zai samar da megawatts 3,050 ga Nijeriya.
A shekarar 2017, majalisar zartarwar Nijeriya ta amince da fitar da kudi Dalar Amurka 5.729 kwatankwacin Naira Tiriliyan 1.140 don gudanar da aikin.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata