Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuShugaba Tinubu ya amince da sayen sabbin makaman yaki domin dakile matsalar...

Shugaba Tinubu ya amince da sayen sabbin makaman yaki domin dakile matsalar tsaro

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da sayen karin kayan aikin soja domin karfafa yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a fadin Nijeriya.

Ministan Tsaro, Christopher Musa, ya bayyana hakan bayan ganawar shugaban kasa da hafsoshin rundunonin tsaro, inda ya ce an gabatar wa shugaban rahoto kan yadda ake gudanar da ayyukan tsaro a sassan kasar.

Ya ce duk da hare-haren da aka samu a baya-bayan nan, sojoji sun yi nasarar hallaka wasu manyan kwamandojin ‘yan ta’adda tare da kwace wasu kayayyakinsu, yana mai cewa rundunar sojin Nijeriya na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron al’ummar kasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata