Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuShugaba Tinubu ya shiga ganawar sirri da manyan hafsoshin tsaron Nijeriya

Shugaba Tinubu ya shiga ganawar sirri da manyan hafsoshin tsaron Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu na wata ganawar sirri tare da shugabannin tsaro da Sufeto Janar na ‘yan sanda IGP a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Cikin wadanda ke halartar taron akwai babban hafsan tsaro na kasa, Janar Christopher Musa; babban hafsan sojojin kasa, Janar Olufemi Oluyede; babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar; babban hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla; da kuma sufeto janar na ‘yan Sanda, Kayode Egbetokun.

Duk da cewa cikakken bayani game da taron bai fito ba a lokacin hada wannan labarin kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, amma ana hasashen tattaunawar na da nasaba da sake fasalin tsaro a sassan kasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata