Thursday, April 9, 2026
HomeBabban LabarinmuShugaba Tinubu ya umarci dukkanin rijiyoyin hakar man fetur da suka tsaya...

Shugaba Tinubu ya umarci dukkanin rijiyoyin hakar man fetur da suka tsaya su dawo bakin aiki – Ministan man Fetur

Shugaba Bola Tinubu ya bai wa mamallaka wuraren hakar man fetur da ba sa aiki a Nijeriya umarnin dawo da su kan aiki, a wani yunkuri na farfado da tattalin arzikin man da ke fuskantar barazanar durkushewa.

Umarnin na kunshe ne cikin bayanan da karamin ministan man fetur na kasar Heineken Lokpobiri ya yi a taron mako na ma’adanan mai da iskar gas a birnin Abuja na shekarar 2025.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito Ministan ya ce farfado da wuraren zai taimaka matuka wajen samun zuba hannayen jari a fannin na man fetur daga bangarori da dama, da kuma tabbatar da ci gaba mai dorewa.

Gwamnatin tarayya dai ta sanya kudurin samar da gangar danyen man fetur miliyan 2 da dubu dari a kowace rana, sannan ta ware sama da Naira tiriliyan 84 a kasafin kudin kasar na bana.

Yanzu haka dai, Nijeriya tana iya samar da ganga miliyan 1 da dubu dari 4 ne kawai a rana, kamar yadda tashar Channels TV ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata