Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuShugaba Tinubu ya umurci karin jami’an tsaro a jihar Borno biyo bayan...

Shugaba Tinubu ya umurci karin jami’an tsaro a jihar Borno biyo bayan harin da aka kai a masallaci – Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin rundunonin tsaro na musamman zuwa Maiduguri, Jihar Borno, domin kamo waɗanda suka kai harin bam a masallacin Al-Adum da ke kasuwar Gamboru.

Shettima ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis, bayan harin da ya kashe mutane biyar tare da jikkata wasu a lokacin sallar magariba ranar Laraba.

A cewarsa, Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, ya ba da umarnin ƙara tsaurara matakan tsaro a Borno, yana mai jaddada cewa gwamnati na aiki tare da hukumomin jiha da jami’an tsaro domin kare al’umma da muhimman gine-gine a Arewa maso Gabas.

Shettima ya ƙara da cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunkuri na tayar da zaune tsaye ba, yana mai tabbatar wa ’yan Nijeriya cewa za a hukunta masu hannu a harin bisa doka, tare da jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata