Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedShugaban Zimbabwe ya nada 'ya'yansa biyu mukamin minista a gwamnatinsa

Shugaban Zimbabwe ya nada ‘ya’yansa biyu mukamin minista a gwamnatinsa

Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya nada dan cikinsa David Kudakwashe Mnangagwa mukamin karamin minista bayan sake zabensa da aka yi a matsayin shugaban kasar.
Wannan nadi dai ya tayar da kura a siyasar kasar, inda wasu ke zargin shugaban kasar da nadin ‘yan’uwa da abokan arziki a gwamnatinsa.
An nada David Kudakwashe Mnangagwa mai shekaru 34 a mukamin karamin ministan kudi a yayin da aka nada Tongai Mafidhi, da ga dan’uwan shugaban a matsayin karamin ministan shakatawa na kasar.
Emmerson Mnangagwa dai ya ayyana sunayen mutane 26 da ya nada mukaman ministoci a sabuwar gwamnatin.
A shekarar 2017 dai ne aka fara zaben Mnangagwa mai shekaru 80 a matsayin kasar Zimbabwe.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata