Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya bayyana a ranar Asabar cewa, dakarun sojojin Nijeriya sun halaka wasu manyan kwamandojin ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru a wani gagarumin samame da aka gudanar tsakanin watan Mayu da Yuli, 2025.
A cewar Ribadu, cikin waɗanda aka kashe har da Mahmud Usman, wanda aka fi sani da Abu Bara’a, tare da mataimakinsa Mahmud al-Nigeri da ake kira Mallam Mamuda.
Rahoton jaridar Premium Times ya nuna cewa duka biyun sun shafe shekaru ana neman su ruwa a jallo a matsayin manyan masu laifi.
Abu Bara’a, wanda ya ayyana kansa shugaban Ansaru, shi ne ya kafa ƙungiyoyi a sassa daban-daban na ƙasar tare da jagorantar ayyukan ta’addanci ta hanyar garkuwa da mutane da fashi da makami domin samun kuɗaɗe.
Mallam Mamuda kuwa ya jagoranci wani rukuni a dajin Kainji, inda rahotanni suka ce ya samu horo daga ‘yan jihadi na ƙasashen waje a Libya.
