Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuSoludo na jam'iyyar APGA, ya sake lashe zaben gwamna a Anambra

Soludo na jam’iyyar APGA, ya sake lashe zaben gwamna a Anambra

Gwamna Chukwuma Soludo ya samu nasarar sake lashe zaben gwamnan jihar Anambra na shekarar 2025, inda hukumar zaben Nijeriya INEC,ta bayyana shi a hukumance a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u masu yawa.

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa sakamakon da aka sanar da shi da safiyar Lahadi ya nuna cewa Soludo ya yi nasara a dukkanin kananan hukumomi 21 na jihar.

Farfesa Omoregie Edoba, wanda shi ne jami’in tattara sakamakon kuma Shugaban Jami’ar Benin UNIBEN, ne ya bayyana Soludo a matsayin wanda ya ci zaben.

Soludo, dan takarar Jam’iyyar APGA, ya samu kuri’u 422,664, ya doke babban abokin takararsa Nicholas Ukachukwu na APC wanda ya samu 99,445. Sai Paul Chukwuma na YPP da ya zo na uku da 37,753, sannan George Moghalu na LP da 10,576, yayin da Jude Ezenwafor na PDP ya samu 1,401 kacal.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata