Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiSulhu da 'yan bindiga ba tare da an karbe makamansu ba, hatsari...

Sulhu da ‘yan bindiga ba tare da an karbe makamansu ba, hatsari ne mai girma – Gwamna Dauda

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gargadi gwamnoni da hukumomin tsaro da su guji sulhu da ‘yan ta’adda da ba tare da an karɓe makamansu ba.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sulaiman idris ya fitar Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wani jawabi da ya gabatar a cibiyar nazarin tsaro ta kasa NISS da ke Abuja a ranar Laraba.

Gwamnan ya ce, yaki da ‘yan bindiga a Zamfara ya samo asali ne daga matsalolin tattalin arziki, rashin aikin yi, rikice-rikice da yaduwar makamai daga kasashen makwabta.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa tatttaunawa da ‘yan ta’adda ba tare da an kwace makamansu ba ba dai-dai bane,zaman lafiya yana samuwa ne idan aka yi afuwa tare da karɓe makamansu,domin idan aka barsu da bindigu rikici ba zai kare ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata