DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Wednesday, July 8, 2026
HomeLabaraiSulhu da 'yan bindiga ba tare da an karbe makamansu ba, hatsari...

Sulhu da ‘yan bindiga ba tare da an karbe makamansu ba, hatsari ne mai girma – Gwamna Dauda

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gargadi gwamnoni da hukumomin tsaro da su guji sulhu da ‘yan ta’adda da ba tare da an karɓe makamansu ba.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sulaiman idris ya fitar Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wani jawabi da ya gabatar a cibiyar nazarin tsaro ta kasa NISS da ke Abuja a ranar Laraba.

Gwamnan ya ce, yaki da ‘yan bindiga a Zamfara ya samo asali ne daga matsalolin tattalin arziki, rashin aikin yi, rikice-rikice da yaduwar makamai daga kasashen makwabta.

Gwamna Lawal ya jaddada cewa tatttaunawa da ‘yan ta’adda ba tare da an kwace makamansu ba ba dai-dai bane,zaman lafiya yana samuwa ne idan aka yi afuwa tare da karɓe makamansu,domin idan aka barsu da bindigu rikici ba zai kare ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata