Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedTalakawa sun fasa rumbun adana kayan abinci na gwamnatin jihar Kebbi da...

Talakawa sun fasa rumbun adana kayan abinci na gwamnatin jihar Kebbi da shagunan ‘yan kasuwa, sun kwasa

Wasu mazauna jihar Kebbi sun kai hari a rumbun adana kayan abinci na gwamnatin jihar da ke Bayan Kara cikin kwaryar Birnin Kebbi, inda suka kwashi kayan abinci.

Lamarin kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, ya faru ne a daren Asabar.
Maharan da suka yi kukan-kura suka afka a rumbun, sun kuma fasa wasu shagunan ‘yan kasuwa, suka saci kayan abinci can ma.
Kazalika, sun kuma tare wata tirela makare da kayan abinci da aka ba gwamnatin jihar Kebbi ta kayan abinci, nan ma suka wawashi hatsi.
Da ya ke ganawa da manema labarai, Muhammad Gwadangwaji, wanda shi ne shugaban ‘yan kasuwar na Bayan Kara Birnin Kebbi, ya ce matasan sun kuma banka wuta ga wasu rumbunan adana kaya ‘yan kasuwa.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata