Tallafin da gwamnatin Nijeriya ke biya a kan wutar lantarki ya tashi daga Naira biliyan 610 a 2023 zuwa Naira tiriliyan 1.94 a shekarar 2024, duk da karon farashin Band A da aka yi a watan Afrilu 2024, kamar yadda jaridar The PUNCH ta ruwaito.
Wannan karin yana nufin an samu karuwar kashi 219.67 cikin 100 na kudaden da gwamnati ke kashewa don rage nauyin farashin wuta ga ‘yan ƙasa.
Hukumar kula da bangaren lantarki NERC da wasu masana tattalin arziki sun bayyana cewa karin ya faru ne bayan sakin darajar Naira da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar a watan Yuni 2024, da kuma cire tallafin man fetur, wanda hakan ya haifar da tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki.
A cewar NERC, gwamnati ta kashe jimillar Naira tiriliyan 1.94 domin cike gibin da ke tsakanin farashin hakikanin wuta da kudin da ake karɓa daga wajen jama’a.
Sai dai duk da wannan adadi mai yawa, rahoton ya nuna cewa gwamnati ta biya kawai Naira miliyan 371.34 daga cikin wannan nauyin, wanda hakan ke wakiltar ƙasa da kashi 0.02 cikin 100 na adadin da ake binsu.
Tallafin wutar lantarki da gwamnatin Nijeriya ke biya ya haura Naira tiriliyan 1.9 a 2024 – Rahoton Punch
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
