Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuTinubu bai mayar da Arewa saniyar ware ba – Martanin fadar shugaban...

Tinubu bai mayar da Arewa saniyar ware ba – Martanin fadar shugaban Nijeriya ga Kwankwaso

Fadar Shugaban Kasa ta musanta ikirarin da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi cewa an yi watsi da yankin Arewa a mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Fadar ta bayyana cewa akwai muhimman ayyuka da shirye-shirye da dama da ake aiwatarwa a yankin Arewa a halin yanzu.

Kwankwaso, yayin wani taron tattaunawa kan gyaran tsarin kundin tsarin mulki na 2025 da aka gudanar a Kano ranar Alhamis, inda ya yi gargadin cewa ana karkatar da dukiyar kasa zuwa yankin Kudu, wanda hakan ke kara talauci da rashin tsaro a Arewa.

A martaninsa da ya wallafa a shafinsa na X, mai ba Shugaban Tinubu ahawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa, Sunday Dare, ya kalubalanci ikirarin Kwankwaso.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata