Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedTinubu ya yi abin a zo a yaba da ya nada kwararre...

Tinubu ya yi abin a zo a yaba da ya nada kwararre a shugabancin asusun harkokin noma – Umar Abdullahi Yaya

An bayyana nadin Muhammed Abu Ibrahim a matsayin shugaban asusun kula da ci gaban harkokin noma da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi a matsayin abinda ya dace, wanda zai samar da ci gaba a fannin noman ƙasar nan.
Sakataren kungiyar masu kiwon kaji na jihar
Katsina, Alhaji Umar Abdullahi Yaya, ne ya bayyana hakan ya yin hira da yan jarida a Katsina.
 
Ya ce wanda aka naɗan, kwararren Akaunta ne, wanda ke da kwarewa kan shugabanci na sama da shekaru 25 a bangarorin harkokin kudi da fasaha da aikin gona.
Umar Yaya ya ce Mr Ibrahim shi ne wanda ya kafa wata cibiya mai suna (Sponge Analytics); wacce ka tattara bayanai kan harkokin noma da samar da mafita.
Malam Ibrahim wanda kafin nadin nasa shi ne mataimakin shugaban cibiyar (Livestock247); cibiyar harkoki da ci gaban dabbobi, irinta na farko a Najeriya.
 
Hakazalika, Ibrahim ya kasance memba a kwamitotin zartarwa na kampanoni da dama da suka shafi fasaha da muhalli da aikin gona da sai sauransu.
Alhaji Umar Yaya ya bayyana nadin a matsayin wanda yazo a kan lokaci, kuma mai karfafa gwiwar matasan ƙasar nan baki ɗaya.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata