Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuTinubu yana nan kalau bai sangauta ba, martanin APC kenan ga Peter...

Tinubu yana nan kalau bai sangauta ba, martanin APC kenan ga Peter Obi

Jam’iyyar APC ta ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu bai ɓace ba, kuma bai ki halartar aikinsa ba, duk da maganganun da dan takarar shugaban kasa na Labour Party a 2023, Peter Obi, ya yi kan rashinsa bayyanar shugaban a idon jama’a.

A wata sanarwa da mai magana da yawun APC na Legas, Seye Oladejo, ya fitar, jam’iyyar ta ce Tinubu yana ci gaba da gudanar da manyan al’amuran gwamnati – daga tsare-tsare, tsaro, harkokin diflomasiyya zuwa gyaran tattalin arziki.

Oladejo ya ce shugabanci ba a auna shi da fitowa kullum a kafafen watsa labarai ba, sai dai ingancin matakai da sakamakon ayyukan gwamnati.

A baya bayan nan, Peter Obi ya yi tambaya kan inda Tinubu ys shiga, yana cewa shugaban ya shafe kwanaki 196 a waje a 2025, kuma bai yi jawabi ga ‘yan kasa ba tun December 2025.

Tinubu dai ya isa Abu Dhabi domin halartar gangamin Abu Dhabi Sustainability Week 2026, bayan kammala hutun ƙarshen shekararsa a Turai.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata