Tuesday, April 7, 2026
HomeSiyasaTinubu zai kai ziyara jihar Adamawa a ranar Litinin

Tinubu zai kai ziyara jihar Adamawa a ranar Litinin

Shugaban kasa, Bola Tinubu, zai kai ziyara ta aiki jihar Adamawa ranar Litinin, kasa da sa’o’i 48 bayan irin wannan ziyara da ya kai a jihar Kebbi.

Sanarwar ta fito ne daga hannun Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ranar 15 ga Fabrairu, 2026.

A yayin ziyarar ta yini guda, Shugaba Tinubu zai kaddamar da wasu manyan ayyuka da aka kammala, sannan ya gana da manyan jami’an gwamnati da sarakunan gargajiya na jihar.

Daga cikin ayyukan da za a kaddamar a babban birnin jihar, Yola, da Jimeta, akwai titin Galadima Aminu mai layuka takwas da ke hada Gimba da babban birnin jihar.

Sauran ayyukan sun hada da sabon dakin taro na zamani, gyaran kotun koli ta jihar, sabon ginin ofisoshin gwamnati, da kuma sabunta Gidan Gwamnati.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata