Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedTirela 20 ta shinkafar da gwamnatin tarayya ta ce ta ba jihohi,...

Tirela 20 ta shinkafar da gwamnatin tarayya ta ce ta ba jihohi, ba ta iso hannunmu ba – Gwamnan Gombe

Gwamnatin tarayya ta sa kafa ta shure abin da ta kira ikirarin da Gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya ya yi, na cewa har yanzu jiharsa ba ta karbi tirela 20 ta tallafin shunkafar da gwamnatin tarayyar ta ce ta rarraba wa jihohi ba.

Ministan yada labarai Mohammed Idris a wata hira da BBC Hausa kamar yadda jaridar Premium Times ta rawaito, ya ce babu jihar da ba ta karbi nata kason ba, ya zuwa yanzu.
Ministan ya ce tun makonni biyu da suka gabata aka kammala rarraba wannan tallafin shinkafa ga jihohin. Inda ya kara da cewa kowane Gwamna a Nijeriya ya tabbatar da amsar wannan tallafi ban da Gwamnan na jihar Gombe.
A Talatar makon jiya, aka jiyo Gwamna Mohammed Inuwa Yahaya a lokacin da yake ganawa da kungiyoyin fararen hula a jihar na cewa har yanzu wannan sakon tallafin bai zo hannunsu ba daga gwamnatin tarayya.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata