Tsohon gwamnan jihar Benue Samuel Ortom, ya musanta rahotannin da ke cewa yana shirin tsayawa takarar Sanata a zaɓen shekarar 2027.
Jaridar Punch ta rawaito cewa rahotanni sun bazu a kafafen sada zumunta a ranar Juma’a, inda aka riƙa cewa tsohon gwamnan na da niyyar komawa siyasa.
Ortom, wanda ya mulki jihar daga 2015 zuwa 2023, ya taba tsayawa takarar kujerar sanata a 2023 amma ya sha kaye a hannun tsohon mai taimaka masa Sanata Titus Zam.
