Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedWasu mabiya addinin Kirista sun gudanar ibadar Lahadi a filin zanga-zanga...

Wasu mabiya addinin Kirista sun gudanar ibadar Lahadi a filin zanga-zanga a jihar Plateau

Ɗaruruwan masu zanga-zanga mabiya addinin kirista da suka saba Ibadar Lahadi a Coci, a wannan karon sun gudanar da wadannan addu’o’in nasu a matattarar zanga-zanga da ake a jihar Plateau.

Wannan ibada ta nuna hadin kai a fili, saboda a lokacin da suke wannan ibada mabiya addinin Musulunci ne ke kewaye da su suna basu kariya.

Ɗaya daga cikin limaman Cocin dake jagorantar majami’ar El-Buba Outreach Ministries da ke Jos, Pastor Isa El-Buba ya jaddada bukatar gwamnatin Najeriya ta kawo ƙarshen yunwa da rashin tsaro da suka addabi ‘yan ƙasar.

A ranar Juma’a ma anga yadda mabiya addinin kiristan suka bada tsaro ga Musulumai da ke Sallar Juma’a a lokacin zanga-zanga, wacce aka fara ta ranar Alhamis ɗaya ga watan Agustan nan da muke ciki

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata