Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a zaben 2027.
A wata sanarwa da mai taimaka masa kan hulɗa da jama’a da kafafen sadarwa, Lere Olayinka, ya fitar a ranar Asabar, ya bayyana labarin da wata kafar labarai ta wallafa a intanet a matsayin ƙarya daga mutanen da ba su da abin yi face ɓata suna.
Olayinka ya ce wannan rahoton yunƙuri ne na jawo Wike cikin ce-ce-ku-ce marar tushe, ya kuma jaddada cewa a wajen Wike Bola Tinubu ne kadai har zuwa 2031 Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
A cewarsa, Wike mutum ne mai faɗin gaskiya ba ya da nuku-nuku, waɗanda ke son su ɓata masa suna sun rasa abin faɗa ne kawai.
