Rahotannin da jaridar Daily Trust ta samu sun ce barayin daji sun yi garkuwa da dalibai da ma’aikatan da har ya zuwa ynzu ba a tantance adadinsu a jihar Neja.
Lamarin ya faru ne a makarantar darikar Katilika ta St. Mary’s School, da ke unguwar Papiri a ƙaramar hukumar Agwara ta jihar Neja.
