Kwamitin hadin gwiwa na ‘yan majalisar dokokin Amurka ya sanar da cewa zauren zai gudanar da taro a yau Talata 2 ga watan Disamban 2025, domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya.
Wani bayani da dan majalisa Riley Moore ya wallafa a shafinsa na X, ya tabbatar da cewa taron zai kasance ya kunshi kwamitoci daban-daban tare da sauran ‘yan majalisar.
[contact-form][contact-field label=”Name” type=”name” required=”true” /][contact-field label=”Email” type=”email” required=”true” /][contact-field label=”Website” type=”url” /][contact-field label=”Message” type=”textarea” /][/contact-form]
Bayanin ya kuma yi nuni da cewa taron tattaunawar zai mayar da hankali kan karuwar hare-hare a sassa daban daban na Nijeriya musamman a baya bayan nan, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
