Monday, April 6, 2026
HomeUncategorized'Yan sanda sun yi nasarar cafke wasu mutane uku da ake zarginsu...

‘Yan sanda sun yi nasarar cafke wasu mutane uku da ake zarginsu da kai wa yan bindiga makamai da alburusai a jihar Katsina

‘Yan sanda sun yi nasarar cafke wasu mutane uku da ake zarginsu da kai wa yan bindiga makamai da alburusai a dazukan jihar Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta kama wasu mutane uku da ake zargin suna kaiwa ‘yan bindiga makami makamai da alburusai a dajin Katsina.

Wadanda ake zargin su ne sun hada da Haladu Isah na kauyen Tsaskiya, karamar hukumar Safana, Abubakar Ahmed  Sha’iskawa, Barhim, Katsina; da Adamu Musa Ba’ude a Jamhuriyar Nijar.

a cewar kakakin rundunar ‘yan sandan Katsina, Abubakar Sadiq, kamen ya biyo bayan bayanan da aka samu a ranar 6 ga Afrilu, 2024, a ofishin ‘yan sanda da ke Kaita kan munanan ayyukan mutanen uku.

A wata sanarwa da ya fitar ya ce cikin gaggawar ‘yan sanda sun kai dauki tare da samun nasarar gano wadanda ake zargin tare da cafke su a hanyar Dankama a karamar hukumar Kaita.

an gano wadan da ake zargin a hannunsu da kudi naira miliyan daya da dubu dari biyu da uku (N1,203,000.00k) da ake zargin na alburusai ne

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata