Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedYan yankin Neja Delta basu da dalilin yin zanga-zanga ga Tinubu inji...

Yan yankin Neja Delta basu da dalilin yin zanga-zanga ga Tinubu inji ministan harkokin yankin

 

Ministan harkokin Neja Delta Injiniya Abubakar Momoh yace, al’ummar yankin Kudu maso Kudu ba su da dalilin yin zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu.

Mininstan ya fadi haka ne yayin da yake jawabi ga manema labarai a fadar gwamnati a yau ranar Laraba, Ministan ya ce hakan ya faru ne saboda shugaban kasar ya gudanar da ayyuka da dama da nufin bunkasa yankin ba kawai ba, har ma da karfafa matasa.

Ya kara da cewa, a yankin na Neja Delta, Shugaban kasa ya yi abubuwa da yawa kuma ba ya tunanin duk wani dan yankin Neja Delta zai ga ya dace ya fito ya ce yana zanga-zangar adawa da rashin shugabanci.

Daga karshe yayi kira ga matasan da su ci moriyar ayyukan da gwamnati tay, kada su lalata komai don su ne manyan gobe kuma su zasu ci moriyar su.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata