Hukumar zaɓen Nijeriya INEC ta ce za ta bai wa fursunoni damar kada kuri’a a lokacin zaɓe daga gidajen gyaran hali.
Shugaban hukumar, Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin karɓar bakuncin babban kwanturolan hukumar gidajen gyaran hali ta ƙasa, Sylvester Nwakuche, a hedikwatar INEC da ke Abuja.
Yakubu ya tabbatar da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara, wanda ya bai wa fursunoni ‘yancin yin rajista da kada kuri’a a kowane zaɓe.
