Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuZa mu biya bashin 'yan kwangila nan da 20 ga Disamba -...

Za mu biya bashin ‘yan kwangila nan da 20 ga Disamba – Gwamnatin Nijeriya

Gwamnatin Nijeriya ta sha alwashin kammala biyan bashin da ‘yan kwangila ke bin ta, daga yanzu zuwa ranar 20 ga watan Disamban 2025.

 

Wannan dai na a matsayin wani yunkuri na daidaita lamura, biyo bayan zanga-zangar da ‘yan kwangilar suka fara gudanarwa kan halin da suke ciki.

 

Jaridar Punch ta ruwaito cewa ministan ayyuka na Nijeriya David Umahi ne ya bayar da tabbacin a jihar Nassarawa, inda ya ce shugaba Tinubu ya amince da kafa wani kwamiti da zai bibiya tare da tabbatar da cewa an biya su hakkokinsu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata