Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiZa mu hada kai wajen magance matsalar tsaron da ta addabi Nijeriya...

Za mu hada kai wajen magance matsalar tsaron da ta addabi Nijeriya – sabbin hafsonshin tsaron Nijeriya

Sabbin hafsoshin tsaron Nijeriya sun ce za su yi aiki tare domin magance dukkan barazanar tsaro a faɗin kasar, tare da kare martabar ƙasar a kowane fanni.

Jaridar Daily Trust, ta rawaito cewa Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin sabbin hafsoshin da shugaban Tinubu ya tura dasu don amincewa a ranar Laraba.

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya Janar Oluyede, ya bayyana cewa akwai buƙatar Nijeriya ta kafa masana’antar samar da makamai a cikin gida domin rage dogaro da na kasashen waje.

A cewarsa siyan kayan yaki daga kasashen waje akwai tsada sossai, don haka ya kamata a fara kerasu a gida Nijeriya.

Kazalika ya nemi a sake fasalin rundunar ‘yan sanda don rage nauyin da ake dora wa sojoji wajen gudanar da ayyukan da bai kamata su yi ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata