Sabbin hafsoshin tsaron Nijeriya sun ce za su yi aiki tare domin magance dukkan barazanar tsaro a faɗin kasar, tare da kare martabar ƙasar a kowane fanni.
Jaridar Daily Trust, ta rawaito cewa Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin sabbin hafsoshin da shugaban Tinubu ya tura dasu don amincewa a ranar Laraba.
Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya Janar Oluyede, ya bayyana cewa akwai buƙatar Nijeriya ta kafa masana’antar samar da makamai a cikin gida domin rage dogaro da na kasashen waje.
A cewarsa siyan kayan yaki daga kasashen waje akwai tsada sossai, don haka ya kamata a fara kerasu a gida Nijeriya.
Kazalika ya nemi a sake fasalin rundunar ‘yan sanda don rage nauyin da ake dora wa sojoji wajen gudanar da ayyukan da bai kamata su yi ba.
