Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuZa mu kai ƙarar APC gaban ECOWAS kan musguna wa mambobinmu –...

Za mu kai ƙarar APC gaban ECOWAS kan musguna wa mambobinmu – Jam’iyyar ADC

Jam’iyyar haɗaka ta ADC ta ce za ta kai ƙorafi gaban Ƙungiyar ci-gaban kasashen yammacin Afrika ECOWAS da sauran ƙasashen duniya kan hare-haren da ake ta kai wa mambobinta a sassa daban-daban na Nijeriya.

Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, jam’iyyar ta bayyana cewa irin waɗannan hare-haren sun zama ruwan dare a jihohin da APC ke mulki, abin da ke nuna alamar ƙoƙarin murkushe jam’iyyun adawa kafin babban zaɓen 2027.

Mai magana da yawun jam’iyyar ADC na ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya zargi jam’iyyar APC da hana ƴan adawa damar bayyana ra’ayinsu, yana mai cewa hakan na iya kai ƙasar ga zaɓe mai cike da tashin hankali a shekarar 2027.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata