Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiZaben gundumomin Abuja zai nuna cewa Wike ba shi da goyon baya...

Zaben gundumomin Abuja zai nuna cewa Wike ba shi da goyon baya a birnin tarayya – Sanata Kingibe

Sanata Ireti Kingibe ta bayyana cewa zaben kananan hukumomi da ke tafe a babban birnin tarayya zai zama wani filin gwaji da zai bayyana yadda jama’a ke kallon Ministan Abuja, Nyesom Wike.

A wata hira da aka yi da ita a shirin Political Paradigm na Channels Television, Sanatar mai wakiltar Birnin Abuja ta ce, yawancin mazauna Abuja ba su gamsu da irin jagorancin da Ministan ba, kuma suna jin an ware su daga tsarin mulki da gudanarwa.

Sanata Kingibe ta kara da cewa Wike bai fahimci bukatun jama’ar Abuja ba, kuma bai mayar da hankali kan matsalolinsu, musamman na tsaro da gine-ginen ababen more rayuwa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata