Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuƳan Nijeriya miliyan 34 ke fuskantar barazanar yunwa bayan janye tallafin majalisar...

Ƴan Nijeriya miliyan 34 ke fuskantar barazanar yunwa bayan janye tallafin majalisar dinkin duniya – In ji wani rahoto

Kididdiga ta nuna cewa fiye da mutum miliyan 1.4 da ke zaune a sansanonin ‘yan gudun hijira a yankin Arewa maso Gabas na Nijeriya ke fuskantar barazanar yunwa sakamakon janyewar tallafin agaji daga Majalisar Ɗinkin Duniya.

Rahoton Cadre Harmonisé, wanda gwamnatin Najeriya tare da hadin gwiwar FAO, WFP, da sauran kungiyoyin kasa da kasa suka fitar, ya yi hasashen cewa mutane miliyan 33.1 za su shiga matsanancin rashin abinci tsakanin watan Yuni zuwa Agusta 2025, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Saboda haka, jimillar ‘yan Najeriya da ke fuskantar barazanar yunwa ta haura zuwa miliyan 34.7, adadi mafi girma a cikin shekaru da dama, inda akasarin su ke zaune a jihohin Borno, Yobe da Adamawa, wuraren da rikicin Boko Haram da sauran hare-haren tsaro suka addaba tsawon shekaru.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata