DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaro sun yi ajalin ‘yan ta’addan Lakurawa a jihar Kebbi

-

Nasir Idris 

Rundunar hadin gwiwa ta jami’an tsaro a jihar Kebbi ta yi nasarar halaka wasu da ake zargin ‘yan Lakurawa ne, yayin da wasu da dama suka tsere da raunuka, a wani sumame da suka kai a kauyukan Rubin Bisa da Fana da ke karamar hukumar Dandi a jihar Kebbi.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan tsaro, Abdulrahman Zagga, ya fitar a Birnin Kebbi babban birnin jihar.

Abdulrahman Zagga ya ce an gudanar da aikin ne a ranar Larabar da ta gabata, bisa rahotanni da bayanan sirri da aka samu.

Biyo bayan korafin da shugaban karamar hukumar Dandi, Dakta Mansur Kamba, ya gabatar mako daya da ya gabata, dangane da ayyukan ‘yan bindigar a kauyukan Fana da Rubin Bisa,kuma an kwato manyan makamai daga hannun wadanda ake zargin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara