DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sanar da zaman makoki na kwana uku bayan ‘yan ta’adda sun yi ajalin mutum 44 a masallaci

-

Abdoulrahmane Tiani

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sanar da zaman makoki na kwana uku a kasar  bayan ajalin wasu mutane 44 a kudu maso yammacin ƙasar a wani hari da ake zargin “yan ta’adda” da ke da alaƙa da ƙungiyar ta’addanci ta Daesh suka kai.

Ma’aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar Nijar ce ta sanar da hakan a wata sanarwa da ta fitar a gidan talabijin na ƙasar a ranar Juma’a.

Ma’aikatar ta ce ‘yan ta’addan sun yi ajalin mutanen ne a lokacin da suka afka cikin wani masallaci a ƙauyen Fombita da ke Kokorou inda suka far wa masallata.

Ma’aikatar ta yi Allah-wadai da harin tare da shan alwashin ƙara matsa ƙaimi domin yaƙi da ta’addanci a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ba gasa muke yi da kamfanin NNPCL ba – Dangote

Shugaban Rukunin kamfanonin Dangote, alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa matatar man fetur dinsa ba ta yin gasa da Kamfanin man Fetur na Nijeriya, wato...

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Mafi Shahara