DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

-

 

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027, ko da ba tare da goyon bayan gwamnoni ba.

El-Rufai, wanda kwanan nan ya fice daga jam’iyyar APC mai mulki zuwa jam’iyyar SDP, ya bayyana haka ne yayin wata hira da manema labarai a birnin Kano, inda ya ce dabarar da kawancen ke amfani da ita ita ce ta kai tsaye wajen tunkarar masu kada kuri’a, ba wai dogaro da masu rike da mukaman siyasa ba.

Wannan kalami na El-Rufai na zuwa ne a daidai lokacin da Kungiyar Gwamnonin PDP ta bayyana kin amincewa da kowacce irin hadaka ko kawance a kokarin yin maja da wasu jam’iyyun adawa ke yi kafin 2027.

Sai dai bayan taron da aka gudanar a Ibadan, karkashin jagorancin mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Umar Damagum, da wasu gwamnoni, kungiyar ta nesanta kanta da wannan sabuwar tafiya, tana mai cewa jam’iyyar PDP za ta tsaya da kafafunta har zuwa 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan Amurka na farko a tarihi Robert F. Prevost ya zama sabon Fafaroma

Robert Francis Prevost, dan asalin birnin Chicago a Amurka, an haife shi a ranar 14 ga Satumba, 1955, yana da shekaru 69 a yanzu. An nada...

Bill Gates zai rarraba kaso 99% na dukiyarsa ga jama’ar duniya

Attajirin nan na duniya Bill Gates, ya bayyana aniyarsa ta raba kaso 99% na dukiyar da ya mallaka da ta kai Dala bilyan 200, ga...

Mafi Shahara