DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

-

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu ‘yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da Hamid Mahmoud tsohon wakilin Muryar Amurka (VOA), da Maman Bachir Sani da kuma Masaouda Jaharou Sanda

Malan Anisse daya daya daga cikin shugabannin kafar ya shaida wa DCL cewa tun ranar Alhamis ne aka kama abokan aikin nasu, kuma har yanzu haka ana cigaba da tsare su a ofishin hukumar ‘yan sanda na jihar kafin a gabatar da su a gaban alkali.

Google search engine

An kama wadannan ‘yan jaridar ne dai sakamakon zargin su da bada labarin da ba gaskiya ba, kan cewa hukumomin kasar Nijar sun yanke hulda da hukumomin Rasha da na Turkiyya wanda suka ce su ma sun same shi ne daga wata kafa ta ketare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaban Amurka Donald Trumph ya haramtawa Farfesa Wole Soyinka zuwa kasar

Gwamnatin Amurka karkashin jagorancin shugaba Donald Trump ta soke takardar izinin shiga ƙasar ga Farfesa Wole Soyinka, sanannen marubuci a duniya. Farfesa Soyinka ya bayyana hakan...

Hukumar agajin gaggawa NEMA ta karɓi ƴan Nijeriya 153 da suka makale a Chadi

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA, ta bayyana cewa ta karɓi ’yan Nijeriya 153 da suka dawo daga ƙasar Chadi, ƙarƙashin shirin Ƙungiyar...

Mafi Shahara