Felix Kwakye Ofosu, Ministan Ƙasa mai kula da harkokin sadarwar gwamnati a Ghana, ya sanar da cewa gwamnati za ta ɗauki matakin dakatar da wasu harajin man fetur domin rage radadin tsadar mai da ke addabar jama’a sakamakon tashin farashin mai a duniya.
DW Africa ta ruwaito matakin, wanda zai fara aiki daga mako mai zuwa, cewa zai ɗauki tsawon makonni huɗu kafin a sake duba shi, gwargwadon yadda farashin mai a kasuwannin duniya ke sauyawa, musamman dangane da rikice-rikicen yankin Gabas ta Tsakiya.
