Amurka ta sanar da sabbin takunkumi kan ɓangaren mai na Iran, a wani mataki da ke nuni da ƙara matsa lamba kan tattalin arzikin ƙasar yayin da rikici ke ci gaba a yankin Gabas ta Tsakiya.
Rahotanni sun nuna cewa sabbin takunkumin sun fi mayar da hankali ne kan hanyoyin sufuri da kasuwancin man fetur na Iran, inda aka sanya takunkumi kan mutane, kamfanoni da jiragen ruwa sama da guda ashirin da ke da alaƙa da jigilar man ƙasar.
Hukumomin Amurka sun bayyana cewa wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin da suke yi na dakile hanyoyin da Iran ke bi wajen fitar da man fetur zuwa kasuwannin duniya, wanda shi ne babban tushen kuɗaɗen shiga ga gwamnatin ƙasar.
Bugu da ƙari, Amurka ta kuma yi gargaɗin cewa duk wata ƙasa ko kamfani da ya ci gaba da sayen man Iran na iya fuskantar irin waɗannan takunkumi, matakin da zai iya shafar hulɗar kasuwanci tsakanin Iran da sauran ƙasashe.
Wannan sabon mataki ya zo ne a daidai lokacin da rikicin yankin ya tsananta, musamman bayan rufe mashigar ruwa ta ‘Strait of Hormuz’, wadda ke da matuƙar muhimmanci wajen jigilar mai a duniya.
Masana na ganin cewa wannan mataki na iya ƙara dagula kasuwar mai a duniya, domin duk wani cikas da ya shafi fitar da man Iran na iya janyo hauhawar farashi da kuma rashin daidaito a kasuwannin makamashi.
