Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedBa rikicin masarauta bane dalilin rashin ci gaba da zaman zauren -...

Ba rikicin masarauta bane dalilin rashin ci gaba da zaman zauren – Majalisar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta karyata rade-radin da ake yadawa kan batun zaman majalisar, lamarin da aka jingina da rashin tsaro, wanda ya samo asali daga rikicin masarautar jihar.

Kakakin Shugaban Majalisar, Kamaluddeen Shawai ne ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN a ranar Laraba.

Yace labarin da ake yadawa ba gaskiya bane “karya ne kuma maras tushe”.

Shawai ya bukaci al’ummar jihar da su yi watsi da duk wani rahoton da ke nuni da cewa majalisar ba ta sake bude zauren majalisar saboda rashin tsaro da rikicin masarautar ya haifar.

“Majalisar za ta dawo zamanta nan ba da jimawa ba,” in ji shi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata