DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Malaman jami’ar jihar Kaduna (KASU) sun tsunduma yajin aiki

-

 

Google search engine

Kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, reshen jami’ar Kaduna, KASU, ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani daga ranar 18 ga watan Fabrairu.

Kungiyar ta sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugabanta, Dakta Peter Adamu da sakatarenta, Dokta Peter Waziri, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Nijeriya NAN ya rawaito.

Sanarwar ta ce matakin ya biyo bayan amincewar majalisar zartaswar kungiyar ta kasa. 

Kungiyar ta bayyana daga cikin dalilan shiga yajin aikin da suka haɗa da rashin ingata walwalar ma’aikata da rike musu albashi, wanda ya hada da kashi 60 cikin 100 na albashin watan Satumban 2017 da kuma Mayu zuwa Satumban 2022.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara