DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

-

 

Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

Kungiyar ci gaban kasashen yammacin Afrika ECOWAS ko kuma CEDEAO, na ci gaba shirye-shirye kaddamar da kudin bai daya a yankin mai suna ECO, biyo bayan cimma matsayar da aka yi a yayin taron kasashen karo na 65.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar karshen taron da shugabannin  kasashen suka gudanar karo na 66 a tarayyar Nijeriya Abuja.

A baya dai kungiyar ECOWAS dake da kasashe 15, ta shirya kaddamar da kudin ECK a shekarar 2020, amma cutar korona ta kawo tsaiko inda a halin yanzu aka sanya 2027 a matsayin ranar kaddamarwa.

Hukumar ta ce ta yi amfani da shawararin da babban kwamiti ya gabatar, na zabar kasashe da za a kaddamar da tsarin da kuma wadanda za su shigo daga baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara