Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedA gidan haya nake zaune a Abuja - Dangote

A gidan haya nake zaune a Abuja – Dangote

Hamshakin attajirin nan na Nahiyar Afrika Alhaji Aliko Dangote ya ce gidan da yake zaune a duk lokacin da ya ziyarci Abuja, ba nasa bane, haya yake yi.
Aliko Dangote a wata ganawa da manema labarai a Lagos, ya ce irin himmar da yake da ita na ganin masana’antu sun habbaka a Nijeriya ne ya sa baya da burin gina gidaje a wajen kasar.
Dangote ya bayyana cewa ya taba mallaka gida a birnin London amma ya sayar da shi a shekarar 1996.
Ya ce dalilinsa na kin yin gidaje a Amurka ko Ingila shi ne don ya kafa masana’antu kuma ya rage lokacin da zai rika batawa don ziyarar kadarorin da ya adana a kasashen waje.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata