DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Sunday, April 12, 2026
HomeBabban LabarinmuAn rufe kasuwar Jilli da sojoji suka kai wa hari tun shekaru...

An rufe kasuwar Jilli da sojoji suka kai wa hari tun shekaru 5 da suka wuce — Gwamna Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya ce kasuwar Jilli da ke karamar hukumar Gubio — inda aka kai harin sama da ya yi sanadin mutuwar fararen hula — an rufe ta tun shekaru biyar da suka gabata.

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Malam Dauda Iliya ya fitar, ya ce gwamnan ya bayyana cewa kasuwar ta zama wurin da ake zargin masu aikata laifuka da masu taimaka musu ke amfani da ita.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa gwamnan ya ce ya samu cikakken bayani kan harin saman da rundunar Operation Hadin Kai ta kai a yankin, wanda ke kan iyakar jihohin Borno da Yobe.

Zulum ya kara da cewa gwamnatin Borno na tuntubar gwamnatin Jihar Yobe da manyan hafsoshin soji domin fahimtar abin da ya faru da daukar mataki.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata