DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Monday, April 13, 2026
HomeSiyasaEl-Rufa'i ya ambaci babban taron ADC a cikin kotu

El-Rufa’i ya ambaci babban taron ADC a cikin kotu

An samu wani dan karamin yanayi mai jan hankali a Babbar Kotun Jihar Kaduna a ranar Litinin, yayin da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana yana tattaunawa kan babban taron jam’iyyar ADC da aka shirya yi a ranar Talata.

Jam’iyyar adawa ta ADC ta sha alwashin ci gaba da gudanar da taron duk da gargadin da Hukumar Zabe ta Kasa INEC ta yi na kada a yi shi.

Hotuna:Tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai ya isa kotu kan tuhume-tuhume 10

Sai dai, lokacin da tsohon gwamnan wanda jigo ne a jam’iyyar ADC ya isa kotu da misalin karfe 9 na safe, an ji yana tattaunawa a takaice da daya daga cikin magoya bayansa.

El-Rufai, wanda ya sanya farar babbar riga da hula mai launin toka, yana karanta wata takarda a hannunsa yayin da yake shiga cikin kotun tare da lauyoyinsa.

“Don haka gobe ne taron, ko?” ya tambaya, inda magoyin bayan ya amsa da cewa “In Allah ya yarda.”

Daga nan sai El-Rufai ya yi murmushi ya shiga cikin kotun tare da daya daga cikin matansa.

An tsaurara matakan tsaro a harabar kotun da kuma hanyoyin da ke kaiwa gare ta.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an gurfanar da tsohon gwamnan a gaban Babbar Kotun Jihar tare da wani Amadu Sule kan zarge-zargen da suka hada da amfani da mukami ba daidai ba, zamba, yunkurin aikata zamba da kuma yi wa wani gata ba bisa ka’ida ba.

Wadannan tuhume-tuhume, wadanda Hukumar ICPC ta shigar, sun bambanta da wadanda ke gaban Babbar Kotun Tarayya, inda za a saurari bukatar belinsu a ranar Talata a Kaduna.

Jam’iyyar ADC ta bayyana shari’ar El-Rufai a matsayin farautar ‘yan adawa, tana zargin gwamnatin tarayya da kokarin takura jagororin adawa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata