DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba da gan-gan harin da muke kai wa ‘yan ta’adda ke shafuwar fararen hula ba – Sojojin Nijeriya

-

 Ba da gan-gan harin da muke kai wa ‘yan ta’adda ke shafuwar fararen hula ba – Sojojin Nijeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce duk hare-hare ta sama da take kai wa ga masu aikata laifukan ne ba fararen hula ba.

Babban Hafsan Sojojin Najeriya Janar Christopher Musa ne ya bayyana haka a wata hira da yayi a gidan Talabiji na Arise TV, a lokacin da yake mayar da martani game da mutuwar fararen hula sama da 10 sanadiyar harin da sojojin suka kai kwanan nan a Zamfara.

Janar Christopher Musa, wanda ya bayyana cewa sojoji sun bi ka’idoji masu tsauri kafin aiwatar da duk wani hari ta sama, ya jaddada cewa sojojin na kai hare-hare ta sama daidai gwargwado domin kawar da yan ta’adda dake addabar wasu sassan jihohin Nijeriya.

Leave a Reply to Anonymous Cancel reply

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ba gasa muke yi da kamfanin NNPCL ba – Dangote

Shugaban Rukunin kamfanonin Dangote, alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa matatar man fetur dinsa ba ta yin gasa da Kamfanin man Fetur na Nijeriya, wato...

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun kama wasu ‘yan jarida uku na Radio Sahara da ke jihar Agadez

Rahotanni daga gidan Radio Sahara Fm da ke jihar Agadez sun tabbatar da kama wasu 'yan jaridar gidan radiyon guda uku da suka hada da...

Mafi Shahara