DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotun koli ta tabbatar da Samuel Anyanwu, a matsayin sakataren PDP na Kasa

-

Kotun koli a Nijeriya ta tabbatar da Samuel Anyanwu, kuma na hannun daman ministan birnin tarayya Abuja a matsayin sakataren jam’iyyar PDP na kasa.

Samuel Anyanwu da Sunday Ude Okoye dai sun yi takun-saka tsakaninsu, lamarin da ya janyo rarrabuwar kawuna a tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Sai dai Ude Okoye ya samu goyon baya daga bangarori daban-daban na jam’iyyar wadanda suka dogara da hukuncin da wata kotun daukaka kara da ke zamanta a Enugu ta yanke.

Kotun daukaka karar ta tabbatar da tsige Anyanwu da wata babbar kotun tarayya da ke Enugu ta yi.

Sai dai a wani hukunci da aka yanke a ranar Juma’a, kotun mai alkalai biyar, yayin zartar da hukuncin ta ce al’amuran da suka shafi shugabanci a jam’iyyar siyasa al’amari ne na cikin gida, kuma bai kamata ya zama na kotu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara