DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisa uku daga jihar Katsina sun bar PDP sun koma APC

-

‘Yan majalisar wakila uku daga jihar Katsina sun bar jam’iyyarsu ta PDP sun koma APC.

‘Yan majalisar su ne Ali Iliyasu na Safana/Batsari/Danmusa, Salisu Yusuf Majigiri na Mashi/Dutsi da Abdullahi Balarabe na Bakori/Danja.

Google search engine

Kakakin majalisar wakilan Tajuddeen Abbas ne ya karanta sanarwar ficewar ta su.

‘Yan majalisar dai sun bayyana rikicin da ya addabi jam’iyyar PDP ne ya sa suka bar ta. Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya ziyarci majalisar don gane wa idonsa yadda ‘yan majalisar suka sauya sheka suka koma jam’iyya mai mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara