Wata Likita a Asibitin Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa ta’annati, EFCC, Dakta Marvelous Idemudia, ta nuna damuwa kan yadda ake samun ƙaruwar matasan Najeriya da aka gano suna fama da cutar hawan jini da kuma ciwon sukari.
Dakta Idemudia ta bayyana hakan ne a wata hira da ta yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, inda ta ce cututtukan da a da aka fi danganta su da tsofaffi yanzu suna ƙara yawaita a tsakanin matasa.
