Masu neman takarar gwamnan Jihar Yobe guda shida a ƙarƙashin jam’iyyar APC sun yi watsi da zaɓen tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Baba Mallam Wali, a matsayin ɗan takarar sasanci na jam’iyyar a zaɓen 2027.
’Yan takarar sun bayyana cewa za su amince ne kawai da sahihin zaɓen fidda gwani mai gaskiya da adalci domin zaɓen ɗan takarar gwamna.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa masu neman takarar sun haɗa da Sanata Ibrahim Mohammed Bomai, Bashir Sheriff Machina, Kashim Musa Tumsah, Injiniya Mustapha Yunusa Maihaja, Lawan Kolo Geidam da tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Usman Alkali Baba.
A wata sanarwa bayan taronsu a Abuja, sun ce zaɓen Baba Mallam Wali ya saɓa wa dokar zaɓe da kundin tsarin APC.
Sun jaddada cewa idan za a yi tsarin sulhu, dole ne a bi dukkan tanade-tanaden doka da kundin tsarin jam’iyyar.
Masu neman takarar sun kuma bayyana rashin amincewa da shugaban APC na jihar, Alhaji Mohammed Gadaka, suna zarginsa da nuna son kai a tsarin siyasar da ake gudanarwa.
Saboda haka suka buƙaci a cire shi daga duk wani aiki da ya shafi gudanarwa da sa ido kan zaɓen fidda gwani na gwamna a jihar.
Sai dai sun sake bayyana goyon bayansu ga shugabancin APC na ƙasa tare da marawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya kan sake tsayawa takara.
Rahotanni sun ce wasu masu ruwa da tsaki a siyasar Yobe ne suka amince da Baba Mallam Wali a matsayin wanda ake so ya gaji Gwamna Mai Mala Buni bayan wa’adinsa ya ƙare a 2027.
